Katsina

From Wikipedia, the free encyclopedia

Katsina
Remove ads

Katsina : Mai yiwuwa kalmar daga "Tamashek" (yana nufin ɗa ko jini) ko mazza (maza) tare da "inna" (uwa). Ƙaramar hukuma ce kuma babban birnin Jihar Katsina aArewacin Najeriya. Katsina tana da nisan kilomita 260 km (160 mil) daga gabashin Birnin Sokoto, da kuma kilomita 135 Km (84 mil) daga Arewa Maso Yammacin Birnin Kano, tana kusa da iyakar ƙasar Nijar.

Katsina_State_banner
Thumb
taswirar jihar Katsina
Thumb
Katsina Emir
Thumb
IBB Way
Thumb
Katsina na dukko
Thumb
KATSINA_STATE_INSTITUTE_OF_TECHNOLOGY_AND_MANAGEMENT_KSITM
Thumb
Katsina
Thumb
Hasumiyar Katsina
Fayil:Steel rolling rund-about, IBB Way, Katsina.jpg
Steel_rol
Thumb
National_Museum_Katsina_State_03
ling_round-about,_IBB_Way,_Katsina

An ƙiyasta yawan mutanen dake cikin birnin Katsina a shekara ta 2016 da kimanin mutum 429,000.[1] Birnin akasarin mutanen birnin Musulmai ne daga ƙabilar Hausa da Fulani.

Tsohon shugaban ƙasan Najeriya Umaru Musa Yar'Adua ya kasance babban mutum ne daga Katsina.[2]

Gwamna mai ci na yanzu a Jihar Katsina shine

Umar Dikko Raɗɗa,[3] wanda aka rantsar a matsayin gwamnan jihar a ranar 29 ga watan mayu shekara ta 2023 i

Remove ads

Masarautar Katsina:

Fadar Sarkin Katsina wanda akafi sani da "Gidan Korau" wani katafaren gini ne dake tsakiyar tsohon birnin na Katsina. Fadar ta kuma kasance muhimmin alama na daga al'adu, tarihi da kuma ɗabi'ar Katsinawa.

Kamar yadda tarihi ya nuna, Muhammadu Korau ya gina fadar a shekara ta 1348 CE, wanda ake tsammani cewa shi ne Sarkin musulmi na farko a Katsina. Wannan ne yasa ake kiran masarautar da Gidan Korau. Fadar na ɗaya daga cikin gidan sarauta mafi tsufa kuma na farko-farko, tare da masarautun Daura, Kano Zazzau. Masarutar zagaye take da ganuwa wato katangar gidan sarki wanda a yanzu babu ita. Ƙofar da ke isa zuwa masarautar ita ce 'Ƙofar Soro' sannan kuma ƙofar da ke bayan ta ita ce 'Ƙofar Bai' (babu ita a yanzu). Fadar sarkin a cikin masarautar wani ƙayataccen gini ne mai ƙirar salo na gargajiya.[4] Sarkin Katsina na yanzu shine Alhaji Abdulmumini Kabir Usman, runbun ilimi daga dangin sarakunan Fulani.

Thumb
Fadar Sarkin Katsina
Thumb
Gidan rodi
Remove ads

Tarihi:

Birnin na zagaye da ganuwa mai tsawon kilomita 21 (mil 13) wanda ake tsammani an gina ta a ƙarni na (1100).[5] Kafin zuwan addinin musulunci, jagorar Katsina na musamman shi ne Sarki, wanda yake fuskantar kisa a duk lokacin da aka same shi baya mulki yadda ya kamata. Daga ƙarni na 17 zuwa ƙarni na 18, Katsina ta kasance cibiyar kasuwanci na Ƙasar Hausa kuma ta zamo mafi girma daga cikin ƙasashen Hausa Bakwai. Fulani sun mamaye Ƙatsina a lokacin Jihadin Fulani a shekarar (1807). A shekarar 1903 ne, sarkin Katsina na lokacin Abubakar ɗan Ibrahim ya miƙa wuya ga mulkin Turawa, wadda ta ci gaba har zuwa samun 'yanci kai a shekarar 1960.

Thumb
Katsina a shekarar 1911

A lokacin kasuwancin yankunan kusa da Sahara na Afirka, birnin ya kasance mai albarka kuma muhimmin cibiyar kasuwanci, kuma ana ɗaukanta a matsayin mafi shahara ta fuskar cinikayya, kasuwanci da kuma baiwar sarrafe-sarrafe. Matafiyi ɗan kasar Jamus, Friedrich Hornemann ne bature na farko da ya fara isa birnin a ƙarni na 19.

Tarihin birnin dangane da ilimin boko ya samo asali ne tun daga farkon shekarun 1950, a yayin da aka gina makaranta ta matsakaita ta farko a arewacin Najeriya. Akwai manyan makarantu a yanzu wanda suka haɗa da jami'oi guda biyu, Jami'ar Umaru Musa Yar'adua da kuma ta 'yan kasuwa wato Jami'ar Al-Qalam Katsina; sannan kuma akwai politakanik wato Hassan Usman Katsina Polytechnic da kuma Federal College of Education, Katsina.Har wayau, birnin gida ne ga shahararren masallacin karni na 18 wato Hasumiyar Gobarau, hasumiya mai tsawon mita 15 (50 ft) wanda aka gina da laka da itacen dabino.

Al'amarin Boko Haram na 2020:

A cikin watan Disambar shekara na 2020, aka yi garkuwa da yara 300 'yan makaranta a Ƙanƙara.[6] Amma daga bisani an maido da yara 344 mako ɗaya bayan hakan.[6] Ƙungiyar Boko Haram ta yi iƙirarin cewa ita ta aikata hakan, amma jami'ai sun nuna rashin amincewa da hakan kasancewa babu ƙungiyar Boko Haram a yankin.[7]

Remove ads

Manyan Makarantun Birnin Katsina:

Hotunan Manyan wuraren garin Katsina tare da Makarantu:

Manyan Wuraren Garin Katsina;

Manyan Wuraren Garin Katsina;

Labarin ƙasa:

Yanayi;


Dangane da rabe-raben yanayi na Koppen, Katsina ta faɗa acikin yanayi na zafi wato semi-arid climate, wanda ake rubuta wa a takaice da BSh a taswirorin yanayi na duniya.[8]

Thumb
karamar hukumar katsina

Ruwan sama;

Akwai ƙarancin ruwan sama a birnin Katsina, babu rikodin na ruwa kwata kwata a tsakanin watannin Nuwamba zuwa March.

Ƙarin bayanai S/N, Code ...

Tushe: Hukumar Kula da Yanayi, Katsina (NiMET) 2021.

Yanayin zafi ko sanyi;

Yanayi na nufin yanayi na zafi ko kuwa yanayin sanyi na wuri

Zafi;

Katsina na da yanayi na zafi sosai, tare da watan Aprelu a matsayin wata mafi zafi na kimanin 40.8 °C ko kuma 105.4 °F, tare da yanayi na matsakaicin zafi (31.4 °C or 88.5 °F) acikin watan December.[9]

Ƙarin bayanai S/N, Code ...

Tushe: Hukumar Kula da Yanayi Reshen Jihar Katsina (NiMET), 2021.

Sanyi;

Watan Janairu shi ne wata mafi sanyi a Katsina tare da kimanin 14.7 °C or 58.5 °F.

Ƙarin bayanai S/N, Code ...

Tushe: Hukumar Kula da Yanayi Reshen Jihar Katsina, (NiMET) 2021

Remove ads

Sanannun Mutane;

Hotuna

Manazarta

Loading related searches...

Wikiwand - on

Seamless Wikipedia browsing. On steroids.

Remove ads